Limamin masallacin juma’a na Usman Bn Affan dake Unguwar Gadon Kaya cikin karamar hukumar Gwale a Kano Dr. Abdallah Usman Gadon Kaya ya yi kira mai ƙarfi ga al’umma da su rika taka tsantsan akan yadda yan siyasa ke amfani da su wajen cimma bukatun kashin kansu ya na mai cewa yan Siyasar yanzu bukatunsu ne kawai a gabansu ba na ja’ama ko kare addini ba.
Malamin yaja hankalin yan siyasa musamman daga Arewa su rika kare makomar yankinsu a adaddinance da zaman takewa.
Shiekh Dr. Gadon Kaya ya bayyana cewa sau da yawa, idan aka ga wasu ’yan siyasa suna tayar da jijiyar wuya da sunan kare addini ko wata ƙabila, a zahiri suna kokarin kare muradunsu ne na kashin kai kamar neman mulki,da ɗaukaka ko samun goyon bayan jama’a ba domin cigaban al’umma ba.
Yana wannan jawabi ne Hudubar ta sa kan yadda aka hango wani mutum ya hana wata Daliba sanye da Hijabi shiga dakin rubuta jarabawar shiga manyan makarantu ta kasa JAMB a birnin Ibadan na jihar Oyo.
Duk da cewa JAMB ta magantu akan cece kucen da akayi kan hana dalibar shiga jarabawar, kan cewa baya cikin tsarinta na hana mai Hijibi shiga dakin jarabawa , Dr. Abdallah ya nemi abiwa dalibar hakkinta kuma a hukunta wanda ya hana ta jarabawar.
Dr.Abdallah yace wajibi ne yan siyasa na Arewa su rika kare addini musulunci da makomar mutanan da suka zabe su.
Sannan ya yi tsokaci akan wani kirista da yayi batanci ga Annabi Muhammad SAW yana mai cewa ya zama dole a dauki mataki a kansa, kuma ya tunatar da cewa idan hakurin musulmai ya kare akan yadda ake taba martabar Annabi Muhammadu SAW sai zama a Najeriya ya gagari kowa, musamman su shugabanni.
Malamin ya kuma yi gargadin cewa su na sane da yadda ake cigaba da kulla makirci ga adddinin musulunci a Najeriya daga kasashen waje, inda yace kada hakurin musulmai yaje karshe.
Haka kuma, ya shawarci jama’a da su rika amfani da hankali da ilimi wajen tantance maganganu da manufofin ’yan siyasa, su guji zama kayan aiki a hannun masu son anfani da su wajen cimma burinsu.
A ƙarshe, Dr. Abdallah Gadon Kaya ya tunatar da shugabanni da alumma cewa suji tsoron Allah su gyara ayyukansu wanda shine abokin zamansu a kabari idan mutum ya koma ga Allah.

