Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya kaddamar da aikin gina manyan makarantu guda biyu (mega schools) a Karamar Hukumar Hawul a ranar Laraba, a wani bangare na shirinsa na bunƙasa ilimi a jihar.
Ɗaya daga cikin makarantu ita ce Babbar Kwalejin Ilimin Musulunci (High Islamic College) mai ɗakunan karatu 48, wadda ke garin Shafa. Za a gudanar da karatun ne bisa manhajar Hukumar Kula da Ilimin Larabci da Musulunci ta Ƙasa (NBAIS), domin samar da cikakken ilimin Musulunci na zamani.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/gwamna-zulum-na-borno-ya-amince-a-sayar-da-man-fetur-naira-600-duk-lita-daya-a-jihar/
Gwamna Zulum ya ce gina kwalejojin Ilimin Musulunci na daga cikin alkawuran yaƙin neman zaɓensa, da nufin haɗa ilimin boko da na Musulunci, tare da bai wa ɗalibai damar koyon fasahar zamani, ƙididdiga, karatu da rubutu, da ƙwarewar sana’o’i.
Makarantar ta biyu da aka kaddamar tana garin Marama, wadda za ta taimaka wajen faɗaɗa ingantattun cibiyoyin ilimi a dukkan ƙananan hukumomin jihar.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/gwamna-zulum-ya-nemi-jamaar-borno-su-tashi-da-azumin-ranar-litinin/
Gwamnan ya kuma sanar da shirin ɗaukar ƙarin malamai, inda ya ce:
“Na yi farin cikin aza harsashin ginin makarantar Marama. Wannan gwamnati za ta ba ku cikakken goyon baya. Za mu gina gini mai bene biyu da ɗakunan karatu 36 da sauran muhimman kayan aiki.
Saboda ƙarancin malamai, dole ne mu ɗauki ƙwararrun malamai ‘yan asalin Marama domin koyarwa.”
Kwamishinan Ilimi, Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire, Injiniya Lawan Abba Wakilbe, ya taimaka wajen aza harsashin ginin.
Haka kuma, Gwamna Zulum ya kai ziyara Asibitin Ƙasa na Kashi da Gyaran Gabobi (National Orthopaedic Hospital) da ke Azare, wanda gwamnatin jihar ta gyara domin hanzarta fara ayyukansa.
Bugu da ƙari, gwamnan ya kaddamar da wasu ayyuka a Karamar Hukumar Hawul, ciki har da katafaren shagon kasuwanci (shopping complex) da rumfunan kasuwa.
Gwamnan ya samu rakiyar Sanata Mohammed Ali Ndume (Borno ta Kudu), tsofaffin Mataimakan Gwamna Usman Mamman Durkwa da Ali Abubakar Jatau, Hon. Bukar Talba, Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Hon. Abdullahi Musa Askira, ‘yan majalisar dokoki, kwamishinoni, shugabannin ƙananan hukumomi, da sauran masu ruwa da tsaki daga Kudancin Borno

