Close Menu
  • Shafin Farko
  • Labarai
  • Ketare
  • Siyasa
  • Noma da Kiwo
  • Yanayi
  • Tsaro
  • Karin Wasu
    • Kasuwanci
    • Ilimi
    • Nishadi
    • Muhalli
    • Lafiya
    • Ra’ayi
    • Wasanni
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp Telegram
TST HAUSATST HAUSA
  • Shafin Farko
  • Labarai

    Malaman Addinin Musulunci Daga Jihohin Arewa 19 Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu A 2027

    August 23, 2026

    Hukumar Shari’a ta Kano Ta Wayar da Kan Jama’a Muhimmancin Kalandar Musulunci

    August 22, 2026

    Tinubu ya bada hutu Albarkacin ranar Haihuwar Annabi Muhammadu SAW

    August 21, 2026

    Tunda Farko dama Tinubu ya nemi INEC tayi Adalci.

    August 16, 2026

    HUDUBA : “Na Rantse da Allah, Allah Zai Tambayi ’Yan Kasuwa Kan ’Ya’yansu Saboda Rashin Ba Su Lokaci” — Dr. Abdullah Gadon Kaya

    August 14, 2026
  • Ketare

    Yau Ake Toshe Shafukan Sada Zumunta na Yara yan Kasa da Shekara 16 a Australia

    December 4, 2025

    Rikicin Gaza:Sarkin Saudiyya ya amincewa Falasdinawa 1000 su shiga kasar su sauke farali kyauta

    May 19, 2025

    Duk wanda ya yarda zai bar Amurika ya koma kasarsa zamu bashi kyautar Dala 1000 – Inji Trump

    May 6, 2025

    Ba a ga jinjirin watan Shawwal a Saudiyya ba

    March 29, 2025

    An ga watan Sallah karama a Saudiyya

    March 29, 2025
  • Siyasa

    Wasu ‘Yan Siyasa a Kano Sun Shawarci Kwankwaso Ya Koma PRP Ko Ya Huce Haushi

    June 26, 2026

    Kotu ta soke hukuncin da Ya bai wa NDC matsayin halastacciyar Jam’iyyar Siyasa a Najeriya

    June 26, 2026

    Jar Hula Dai Ta Malam Aminu Kano Ce, Don Haka Ba Za Mu Cire Ta Ba — Gwamna Yusuf

    June 25, 2026

    Na Rungumi Kaddara kan Rasa Takarar Kujerar Majalisar Tarayya a Gezawa da Gabasawa – Hon. Dan Malam

    May 8, 2026

    Kofa Har Yanzu a Buɗe Take ga Kwankwaso Ya Koma PRP, Tunda Akwai Shakkun Samun Mafita a NDC – In Ji Ali Rabiu Ali

    May 4, 2026
  • Noma da Kiwo

    Za’a samu ƙarancin shinkafar Basmati da Indiya ke nomawa a bana

    September 4, 2025

    Tsadar rayuwa: Komai matsayin mutum a Najeriya ya koma gona,saboda abinda na hango -Inji wani Lauya

    December 15, 2024
  • Yanayi
  • Tsaro

    Yan Bindiga Sunyi garkuwa da ’yan uwan Mataimakin Gwamnan Sokoto

    May 1, 2026

    An Kama Budurwa da Kunkuru 30 a Filin Jirgin Sama Ta Na Ƙoƙarin Shiga Jirgi da Su

    April 30, 2026

    A Wasan Hausa na koyi yadda ake sace Mutane – In ji Matashin da DSS suka kama a Kano

    February 13, 2026

    Duk wanda ya Kashe Wani a nemi shawarar Malamai a aika shi Lahira Kawai – Sheikh Daurawa

    January 18, 2026

    An sako Yan Mauludi 28 da aka sace tun 2025 a Filato

    January 10, 2026
  • Karin Wasu
    1. Kasuwanci
    2. Ilimi
    3. Nishadi
    4. Muhalli
    5. Lafiya
    6. Ra’ayi
    7. Wasanni
    8. View All

    Kamfanin Milo Ya Tallafa wa Masu Sana’ar Shayi 2,000 da Kayan Aiki a Kano da Jos

    August 23, 2026

    Gwamna Yusuf Ya Tallafa wa Matasa 1,116 Masu Tallace-Tallace da Masu Faci da Jarin Naira Dubu 50 Kowannensu

    July 23, 2026

    Yan Najeriya basa shayin kashe Kudi, sunyi amfani da Fetur na Naira Tiriliyan 1.58 a Bikin Kirsimeti -In Ji Gwamnatin Tinubu

    January 22, 2026

    Dangote ne ya rage farashin fetur da kaso 5.6%, shi ya sa farashi ya sauka ba saboda janye harajin 15% ba.

    November 19, 2025

    Masanin Kimiyyar Yanayi Daga Kano Dr. Salisu Ya Shiga Jerin Fitattun Masu Bincike na Duniya

    August 18, 2026

    Ya ce Yana Daukar Daliban A Matsayin ‘Ya ‘Yansa

    August 13, 2026

    Sabon Albashin Zai Fara Aiki A Watan Satumba

    August 10, 2026

    Na Amince Gwamna Yusuf Ya Kafa Tarihi a Bangaren Ilimi a Kano — In Ji Tsohon Kwamishinan Ilimi, Hon.Sunusi Kiru

    July 19, 2026

    An Amince da Fara Shirya Fim ɗin Maitatsine – Darakta

    January 9, 2026

    Karamin Yaron da Kakarsa Ta yi Sanadiyar Daukakarsa a Duniya ya Cika Shekara 12

    December 14, 2025

    MUTU KA RABA — HISBA ta ce aure tsakanin Mai Wushirya da ‘Yar Guda ba ta dauke shi da wasa ba

    October 21, 2025

    Majalisar Yara: Gwamna Yusuf ya baiwa yara aron zaman majalisar zartaswarsa a Kano dan girmama Ilimi

    January 13, 2025

    Majalisar dokokin Kano ta amince da dokar cin tarar kuɗi ga duk wanda ya sake tofar da yawu ko majina akan hanya

    February 3, 2025

    Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta dauki sabbin matakan kare Muhalli

    January 31, 2025

    Daga yanzu an daina barin tilin shara akan titunan birnin Kano – Gwamnatin Kano

    January 13, 2025

    Gwamnan ya kai Ziyarar ne Cikin Dare.

    August 16, 2026

    Likitoci Su Daina Ƙaura Zuwa Ƙasashen Waje, Najeriya Na Buƙatar Su – Dr. Habib

    July 23, 2026

    Da ’Yan Najeriya Sun San Haɗarin Abincin da Ake Shanyawa a Gefen Hanya, Ko Kyauta Aka Ba Su Ba Za Su Ci Ba — Masana

    January 30, 2026

    WHO Ta Yi Kira Da A Kara Haraji Kan Barasa Da Abubuwan Sha Masu Dauke Da Sikari

    January 14, 2026

    “ADC Ba Ta Da Karfin Kuri’a a Kudu maso Yamma, Atiku Ya Kamata Ya San Da Haka” — Hon Shehu Isah

    August 16, 2026

    Ya kamata Hisba da Malamai a Kano su bayyana matsayinsu kan yadda yan siyasa ke jifan juna da kalmar LUWADI – Anas Hassan

    February 24, 2025

    Labarin dan Jaridar da ya kafa tarihi a duniyar yada labarai a kafar sadarwa ta zamani

    February 3, 2025

    Burinmu a yanzu shine Barau FC ta samu gurbin shiga gasar zakarun Nahiyar Africa – DSP Barau

    February 25, 2025

    An karrama jagoran kwallon kafa na Barau Jibiril Academy da lambar gwarzon shekara a bangaren Shugabanci

    December 21, 2024

    Kamfanin Milo Ya Tallafa wa Masu Sana’ar Shayi 2,000 da Kayan Aiki a Kano da Jos

    August 23, 2026

    Malaman Addinin Musulunci Daga Jihohin Arewa 19 Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu A 2027

    August 23, 2026

    Hukumar Shari’a ta Kano Ta Wayar da Kan Jama’a Muhimmancin Kalandar Musulunci

    August 22, 2026

    Tinubu ya bada hutu Albarkacin ranar Haihuwar Annabi Muhammadu SAW

    August 21, 2026
TST HAUSATST HAUSA
Home » Ya ce Yana Daukar Daliban A Matsayin ‘Ya ‘Yansa
Ilimi

Ya ce Yana Daukar Daliban A Matsayin ‘Ya ‘Yansa

By tstAugust 13, 20263 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
IMG 20260813 WA0027

Daga Kabiru Muhammad Getso.

Shugaban riko na kwalejin Fasaha ta Husaini Adamu Federal Polytechnic Kazaure, Injiniya Dakta Bashir Ahmad Danzomo, ya bayyana alfaharinsa da daliban kwalejin bisa yadda suke samun nasara a karatunsu da kuma ci gaba da karatu a manyan jami’o’i da sauran manyan makarantu a sassan Najeriya.

Engr. Dr. Bashir Ahmad Danzomo ya ce wannan nasara ta samo asali ne daga jajircewar kwalejin wajen tabbatar da ingantaccen tsarin koyo da koyarwa, tare da samar da yanayi mai kyau da zai bai wa dalibai damar samun ilimi mai inganci.

Ya bayyana cewa kwalejin tana da sassa shida na ilimi, wadanda kowannensu ke da kwasa-kwasai daban-daban da ake koyarwa bisa tsarin da hukumomin da suka dace suka amince da shi.

Shugaban kwalejin ya shaida hakan ne a ofishinsa a lokacin zantawa da manema labarai inda ya ce baya ga shirye-shiryen karatu, makarantar tana da kwararrun malamai da suka samu horo na musamman, wadanda ke amfani da kwarewarsu wajen bai wa dalibai ilimin da ya dace da bukatun zamani.

Ya kuma yi kira ga daliban da suka samu gurbin karatu a kwalejin da su dauki karatunsu da muhimmanci, su kasance masu jajircewa da bin doka da oda, domin ilimin da suke samu a yau shi ne ginshikin makomarsu da ta al’umma baki daya.

Da yake magana kan nasarorin da aka samu tun bayan da ya karbi ragamar shugabancin riko na kwalejin, Engr. Dr. Bashir ya ce ya samu cikakken hadin kan malamai da sauran ma’aikata wajen gano manyan matsalolin da ke fuskantar makarantar da kuma daukar matakan magance su.

Ya ce daga cikin abubuwan da aka fara mayar da hankali a kansu akwai kara yawan ma’aikata, musamman jami’an tsaro, domin tabbatar da tsaron dalibai da kadarorin kwalejin.

Ya kara da cewa an gudanar da gyare-gyare a wurare daban-daban na makarantar, ciki har da samar da isasshen ruwan sha ga daliban da ke zaune a gidajen kwanan dalibai.

A cewarsa, an kuma kara mayar da hankali wajen tsaftace harabar kwalejin da inganta muhallin makarantar, domin samar da yanayin da zai karfafa sha’awar dalibai da malamai wajen gudanar da harkokin koyo da koyarwa.

A wani bangare, Shugaban kwalejin ya yabawa Sanatan Jigawa ta Arewa maso Yamma, Sanata Babangida Husaini Walin Kazaure, bisa irin gudunmawar da yake bai wa makarantar.

Ya ce Sanatan ya taimaka wajen samar da wani katafaren bangare na kwalejin tare da samar da kayayyakin da ake bukata, wanda ya ce hakan zai kara bunkasa harkokin ilimi a makarantar.

Haka kuma, Engr. Dr. Bashir Ahmad Danzomo ya yabawa shugabannin kananan hukumomin Kazaure, Roni, Gwiwa da Yankwashi, bisa daukar nauyin wasu dalibai daga yankunansu domin ba su damar samun ilimi a kwalejin.

Ya ce irin wannan tallafi ba wai kawai yana taimakawa daliban da suka amfana bane, har ma yana bayar da gudunmawa wajen bunkasa ilimi da samar da kwararrun matasa da za su amfani al’umma a nan gaba.

Shugaban kwalejin ya yi kira ga sauran al’umma, musamman masu hannu da shuni, da kungiyoyi da ‘yan kasuwa, da su ci gaba da tallafa wa harkar ilimi da matasa.

Ya ce zuba jari a ilimi na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen rage matsalar rashin aikin yi tsakanin matasa, tare da samar da makoma mai kyau da kuma rage wasu matsalolin da ke addabar al’umma.

A karshe, Engr. Dr. Bashir Ahmad Danzomo ya jaddada cewa hadin kan gwamnati, makarantu, iyaye da sauran al’umma shi ne ginshikin samun ingantaccen ilimi da samar da matasa masu ilimi, kwarewa da kishin kasa.

Share. Facebook Twitter Email Telegram WhatsApp

Related Posts

Masanin Kimiyyar Yanayi Daga Kano Dr. Salisu Ya Shiga Jerin Fitattun Masu Bincike na Duniya

August 18, 2026

Sabon Albashin Zai Fara Aiki A Watan Satumba

August 10, 2026

Na Amince Gwamna Yusuf Ya Kafa Tarihi a Bangaren Ilimi a Kano — In Ji Tsohon Kwamishinan Ilimi, Hon.Sunusi Kiru

July 19, 2026

Ɗan Najeriya daga Kano ya shiga cikin manyan masana yanayi na duniya ,zai halarci taro a Caribbean

April 28, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

Kamfanin Milo Ya Tallafa wa Masu Sana’ar Shayi 2,000 da Kayan Aiki a Kano da Jos

August 23, 2026

Malaman Addinin Musulunci Daga Jihohin Arewa 19 Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu A 2027

August 23, 2026

Hukumar Shari’a ta Kano Ta Wayar da Kan Jama’a Muhimmancin Kalandar Musulunci

August 22, 2026

Tinubu ya bada hutu Albarkacin ranar Haihuwar Annabi Muhammadu SAW

August 21, 2026

Masanin Kimiyyar Yanayi Daga Kano Dr. Salisu Ya Shiga Jerin Fitattun Masu Bincike na Duniya

August 18, 2026
Advertisement
© 2026 TST HAUSA Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.