Daga Ali Rabiu Ali Daddy
Rahotanni daga garin Rimin Zakara na cewa Jami’an tsaro sun harbe mutane 7 tare da raunata wasu 16 a lokacin da suke rushe gidaje a garin da ake cewa mallakin jami’ar Bayaro ne .
Zuwa Yanzu mutane 2 ne suka mutu a cikin mutane 7 da aka harba a garin na Rimin Zakara da ke karamar hukumar Ungogo.
Kuma tuni akayi Jana’izarsu a safiyar ranar Litinin.
Daga cikin wadanda suka jikkata a harbin bindigar harda kananan yara,yayinda kuma wadanda suka mutu ,daya ya kasance matashi dayan kuma magidanci mai yawan iyali.
Shaidar gani da ido Ali Rabiu Ali Daddy ya shaidawa TST cewa an rushe gidaje sama da 20.
A cewar mazauna rimin Zakara a yanzu haka rusau din ya shafi turjiya saboda yadda mutanan garin suka fusata wanda hakan yasa aka harbi wasu ,suka mutu wasu suka jikkata.
Tun a daren jiya jami’an tsaron suka dira a garin na Rimin Zakara inda Kai tsaye suka rushe gidajen jama’a daga bisani al’umar garin suka fara ihu ga jami’an tsaron.
TST Hausa ta rawaito cewa an shafe sama da shekara 20 ana takaddama tsakanin mutanan garin na Rimin Zakara da bangaren jami’ar Bayaro kan asalin Wanda ya mallaki filayen da jama’ar garin suke zaune,duk dacewa jama’ar ta Bayaro bata yi Karin haske ba akan batun a baya bayan nan.
Tawagar jami’an tsaro daban daban ne ciki harda na hukumar Civil defense sukayi dirar mikiya a garin tare da fara rusau,kuma a yayinda aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC) reshen jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa an tura jami’an tsaro da suka hada da NSCDC yankin domin kare kadarorin gwamnati kuma sun fuskanci turjiya daga mazauna yankin.
A yayinda yake zantawa da TST Hausa ,Ma’ajin Kungiyar cigaban al’umar Rimin Zakara Malam Habu Mikailu,yace wannan batu na neman a tashi garinsu na Rimin Zakara yana gaban kotu tun shekarar 2017.
Malam Habu yace korafin nasu yana gaban babbar kotun jihar Kano.
Habu ya jaddada cewa har Yanzu garin Rimin Zakara nasu ne halak malak bana jami’ar Bayaro ba ,duk da kashe yan uwnasu da jami’an tsaro sukayi.
A kalla motoci 30 na jami’an tsaro ne suka dira a garinmu ,Kuma Muna nan kan bakanmu ba zamu bari a tashenmu daga garinmu ba,Inji Habu.
Ya roki gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf da ya shiga tsakani.


2 Comments
Muna tare damu TST hausa
Masha Allah