Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da cewa ta kammala sake fasalin jadawalin karatun shekarar 2025/2026, domin tabbatar da cewa dalibai ba za su yi azumin shakarar 2026 a makaranta ba.
A wata takarda ta sake fasallata Jadawalin karatu da ma’aikatar Ilimi ta jihar ta fitar a yau, an bayyana cewa sabon tsarin zai daidaita lokutan zangon karatu da hutun azumi, tare da kawar da yiwuwar dalibai su yi azumi a cikin makarantu.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/gwamnatin-kano-ta-shiryawa-matasan-da-suka-karbi-musulunci-taron-buda-baki/
Ma’aikatar ta ce an dauki matakin ne domin kare lafiyar ɗalibai, da kuma ba su damar gudanar da ibadar azumi cikin kwanciyar hankali a gida.
Ta kara da cewa wannan canjin ya biyo bayan tattaunawa tsakanin gwamnati,da masu ruwa da tsaki a fannin ilimi, da shugabannin addini.
Gwamnatin ta kuma shawarci iyaye da malamai su taya ta wajen tabbatar da cewa sabon jadawalin ya gudana cikin nasara.
Ana sa ran fara Azumin bana na shekarar musulunci ta 1447 a tsakanin ranar 17 ko 18 ga watan Fabareru na 2026.
A cikin Jadawalin Wanda TST Hausa ta yi nazari akai ,ta gano zangon Karatu na biyu zai fara ne daga ranar Lahadi 18 ga watan Janairu na shekarar 2026 Kuma za’a rufe makarantu a Kano ranar 18 ga watan Fabareru .
Sanarwar tace za’a kammala hutun Sallah a ranar 21 ga watan na Maris.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/ramadangwamnatin-kano-ta-bada-umarnin-kara-lokacin-rufe-kasuwanni/
Haka Kuma za’a koma a cigaba da karatun zango na biyu daga ranar 22 ga watan Maris zuwa ranar 18 ga watan Afirilun 2026 da za’ayi hutun zangon karatun na tsawon mako biyu.

