Shugabannin zartarwa na jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a mazabar Gargari Ward, da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano, sun sanar da tsige Shugaban Jam’iyyar NNPP na Jihar Kano, Hashimu Dungurawa, daga jam’iyyar.
Matakin ya biyo bayan kudurin da mambobin zartarwa 27 na mazabar suka amince da shi, a yayin taron zartarwa na biyu da aka gudanar makonni biyu bayan sake zabensa.
Taron ya gudana ne karkashin jagorancin Shugaban mazabar , Shuaibu Hassan, tare da Sakatarensa Yahaya Saidu Dungurawa.
A cewar kudurin, an tsige Hashimu Dungurawa ne bisa zargin haddasa rarrabuwar kai a cikin jam’iyya, da tayar da rikice-rikicen cikin gida, da gazawar biyan kudaden jam’iyya, da kuma furta kalaman batanci ga Gwamnan Jihar Kano.
Shugabannin mazabar sun bayyana cewa irin wadannan ayyuka sun sabawa ka’idojin jam’iyya, kuma suna lalata martaba, hadin kai da cigaban NNPP a jihar.
Sun jaddada cewa an dauki matakin ne cikin bin kundin tsarin mulkin jam’iyyar, domin tabbatar da da’a, zaman lafiya da hadin kai a cikin jam’iyyar.
Haka kuma, sun ce an aika kwafin kudurin tsige shi zuwa ga shugabannin jam’iyyar a matakan Karamar Hukuma, Jiha da kuma Kasa, domin daukar matakan da suka dace.
Bugu da kari, an sanar da jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da kuma Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, domin sani da bayar da umarnin da ya dace.
Shugabannin Gargari Ward sun ce wannan mataki zai zama izina ga duk wanda ke amfani da mukaminsa ba bisa ka’ida ba, ko kuma yake ganin ya fi dokoki da ladabtarwar jam’iyya karfi.
A karshe, sun sake jaddada biyayyarsu ga jagorancin NNPP na kasa karkashin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tare da cikakken goyon baya ga Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, suna kuma tabbatar da kudirinsu na kare zaman lafiya, hadin kai da ci gaban jam’iyyar a dukkan matakai.

