An kiyasta cewa gamnatin trayyar Najeriya ta kashe sama da naira tiriliyan bakwai a bangaren wutar lantarki tun daga shekarar 2013, lokacin da aka mika bangaren ga kamfanoni kansu domin inganta samar da wuta a ƙasar nan.
Sai dai duk da wadannan kudade da aka kashe , Najeriya har yanzu na fama da matsananciyar matsalar rashin ingantacciyar wutar lantarki.
A cikin watan farko na shekarar 2026 kadai, sau biyu manyan biranen ƙasar suka fada cikin duhun wuta sakamakon faduwar layin wutar ƙasa baki daya.
A wasu gwamnatocin baya, samar da wuta ya taba faduwa zuwa megawatt dubu daya da dari takwas, yayin da bangarorin isar da wuta da rarrabawa ke fama da babbar matsala sakamakon tsofaffin kayan aiki da rashin kulawa.
Ko da yake matsalar wutar lantarki ta dade kafin shekarar 1999, dawowar mulkin dimokuradiyya ya bai wa ’yan Najeriya fata cewa bangaren zai farfado bayan bude shi ga masu zaman kansu.
A kokarin cimma hakan ne aka kafa Dokar Gyaran Bangaren Wutar Lantarki a shekarar 2005, wadda ta sauya tsohuwar Hukumar Wutar Lantarki ta Ƙasa zuwa Kamfanin Riƙon Wutar Lantarki na Najeriya, mai kunshe da kamfanonin samar da wuta guda shida, isar da wuta guda daya da rarrabawa goma sha daya.
A shekarar 2013 ne aka mika wadannan kamfanoni gaba daya ga kamfanoni masu zaman kansu, amma matsalolin bangaren sun ci gaba da ta’azzara.
Tun daga 1999 zuwa yau, kusan dukkan gwamnatocin da suka shude sun dauki gyaran bangaren wuta a matsayin babban ginshiki na manufofinsu, ganin muhimmancinsa ga bunkasar tattalin arziki.
Sai dai alkawuran ministoci daban-daban na kawo karshen katsewar wuta sun gaza cika, inda akasin haka, rugujewar layin wuta ke kara yawaita.
Gwamnatoci sun dauki rance da dama tare da shirye-shirye masu tsada, ciki har da yarjejeniyar wuta da aka kulla a shekarar 2018, wadda aka yi niyyar kara samar da wuta zuwa megawatt dubu ashirin da biyar, amma burin bai tabbata ba.
A halin yanzu, kamfanonin samar da wuta na bin gwamnati bashin sama da naira tiriliyan hudu, suna cewa kudaden tallafi ne da aka yi musu alkawari tun lokacin da aka mallakar bangaren.
Masana sun danganta matsalar da rashin cikakken mallakar bangaren da aka yi, inda gwamnati ke da kaso a kamfanonin rarrabawa tare da rike bangaren isar da wuta. Sun ce hakan na janyo ci gaba da biyan tallafi, rashin gaskiya a lissafi da kuma karuwar bashin da ke addabar bangaren.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/ko-a-fadar-white-house-ta-amurika-ana-amfanin-da-lantarki-na-sola-balle-najeriya-fadar-shugaban-kasa-tayi-martani/
Haka kuma, matsaloli kamar cin hanci, rashin tsayayyen tsari, satar wuta, lalata kayan aiki da rashin jajircewar siyasa sun kara raunana bangaren.
A bangaren mafita, ana samun sabanin ra’ayi kan shirin cire kudin tallafin wuta daga rabon kudaden tarayya na jihohi da kananan hukumomi. Wasu na ganin hakan zai taimaka wajen rage gibin kudade, yayin da wasu ke kallon hakan a matsayin tauye hakkin jihohi da kuma sabawa kundin tsarin mulki.
A gefe guda kuma, ’yan kasa na ci gaba da nuna damuwarsu, inda da dama ke ganin wutar lantarki ta zama alatu maimakon hakki, duk da irin rawar da take takawa wajen rage talauci da bunkasa tattalin arziki.
Duk da tarin kudade, manufofi da alkawura, bangaren wutar lantarki a Najeriya na ci gaba da fama da tsofaffin matsaloli, lamarin da ke haifar da tambayar ko gyaran da aka yi bai wuce sauya suna da tsari ba.

