Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, a bisa umarnin da babban Sufeton ’Yan Sanda na kasa ya bayar IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ta samu nasarar kama matasa uku da ake zargi da kisan wata matar Aure da yayanta guda shida a unguwar Chiranci Kwari dake karamar Hukumar Gwale a Kano.
A wani simame da yan sanda suka kai karkashin umarnin Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori,yan sandan sun kama matasa uku da ake zargi su ne suka shirya aiwatar da wannan mummunan aiki na unguwar ta Chiranci.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/rundunar-yan-sandan-najeriya-ta-ragewa-jamiinta-matsayi-saboda-bada-tsaro-ga-wani-mutum/
Wadanda aka kama sun hada dab Umar Auwalu mai shekaru 23, dan unguwar Sabuwar Gandu, da Isyaku Yakubu wanda aka fi sani da “Chebe”, mai shekaru 40, dan unguwar Sagagi, da Yakubu Abdulaziz wanda aka fi sani da “Wawo”, mai shekaru 21, dan unguwar Sabon Gida Sharada, Kano.
A wata Sanarwa da rundunar yan sandan Kano ta fitar ta ce an kama matasan ne a yayin wani sumame na musamman da aka gudanar daga karfe 10:00 na dare a ranar 17 ga Janairu, 2026 zuwa karfe 4:00 na asuba a ranar 18 ga Janairu, 2026.
Binciken farko ya nuna cewa babban wanda ake zargi, Umar Auwalu, wanda yake dan uwa ga matar da aka kashe (dan yayarta), ya amsa aikata laifin.
Haka kuma matashin Umar yace shine ya taba jagorantar kisan gilla ta hanyar kone wasu matan aure guda biyu a unguwar Tudun Yola, Kano.
TST Hausa ta rawaito cewa a ranar 14 ga watan Nuwamba na shekarar 2025 ne al’ummar unguwar Tudun Yola dake karamar hukumar Gwale a jihar Kano, suka tashi da jimamin mutuwar wasu matan aure biyu, da ake zargin wasu batagari ne suka yi musu kisan gilla sannan suka kunna wuta a gidan.
Rahotanni na cewa wadanda ake zargin sun shiga gidan fuskokinsu a rufe, inda suka dibi man fetur, a cikin injin janareta sannan suka kunna Wuta tare da sossokawa matan auren makamai a wasu sassan jikinsu.
Matan da aka halaka, sun hada da Hauwa’u Yakubu da kuma Zahra’u Aliyu, wadanda dukkansu mata ne ga, Alhaji Ashiru Shu’aibu Usaini.
Matashin dai bai musa ba ya amsa laifinsa a yanzu a wajen yan sanda.
KARI LABARAI:https://tsthausa.com/kisan-gillar-edoni-mutumin-kano-neba-zan-bari-a-cutar-da-kano-ba-ina-baiwa-kanawa-hakuri-inji-gwamnan-edo/
Abubuwan da rundunar ta samu daga hannun wadanda ake zargin sun hada da kayan sawa dake dauke da jini da wayoyin salula guda biyu mallakin marigayyar,da adda, da gora, da wasu kudade da ake zargin an kwace su daga wajen aikata laifin, da kuma wasu muggan makamai.
Bincike na ci gaba da gudana domin gano karin bayanai.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta yabawa jami’anta abisa jajircewa,da kwazo da kwarewar jami’an tsaron da suka gudanar da wannan aiki, tare da gode wa al’ummar jihar bisa addu’o’i, goyon baya, hadin kai da bayanan sirri da suka bayar.
Rundunar ta tabbatar wa jama’a da kudirinta na ganin cewa duk masu aikata laifuka sun fuskanci hukunci bisa tanadin doka.

