Wata Kungiyar yan Jarida ta Kano Concerned Journalist Forum (KCJF) ta sanar da kaddamar da gangamin wayar da kan dalibai yan mata a makarantu mai taken #FlowPioneersKano, wanda aka shirya domin inganta fahimta da kula da lafiyar Al’ada , tare da kawar da kyama da akidu marasa kyau da ke shafar ‘yan mata ‘yan makarantun sakandare a Jihar Kano.
Gangamin na da burin tara kunzugun da mata ke amfani da shi lokacin haila guda miliyan biyar, domin rarrabawa ga makarantun sakandare sama da 200 a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da shugabar kungiyar Hajiya Aisha Ahmed Ismail ta fitar ta ce baya ga rarraba kayan bukata, shirin zai mayar da hankali wajen ilmantar da ‘yan mata kan tsaftar jiki, kula da lafiya yayin haila, da ‘yancin samun ilimi ba tare da tangarda ba, tare da shigar da iyaye da al’umma cikin tattaunawa domin kawar da jita-jita da fahimta mara tushe.
Ta ce gangamin na da muhimmanci wajen kare mutunci da makomar ‘yan mata.
“Lafiyar haila ba batun kunya ba ne, hakki ne.”in ji sanarwar
KARIN LANARAI:https://tsthausa.com/kungiyar-yan-jarida-na-kano-online-ta-taya-waiya-sunusi-bature-da-dan-tiye-murnar-kyautar-da-nuj-ta-basu/
Muna kira ga hukumomin gwamnati, kungiyoyi masu zaman kansu, kamfanoni, da daidaikun mutane masu kishin al’umma da su mara wa wannan shiri baya, domin tabbatar da cewa babu wata yarinya da za ta rasa ilimi ko mutunci saboda kalubalen haila,” in ji ta.
Za a fara aiwatar da gangamin a ranar 19 ga Janairu, 2026, inda za a fara rarraba pad na haila a makarantun sakandare fiye da 50 a mataki na farko.
Haka kuma, za a gudanar da tattaki domin Wayar da Kai a ranar 27 ga Janairu, 2026, daga makarantar Government Technical College zuwa Gidan Gwamnatin Jihar Kano, domin kara jawo hankalin al’umma kan muhimmancin lafiyar haila.
KARIN LANARAI:https://tsthausa.com/ranar-kare-yancin-dan-adam-zamu-fara-hukunta-matan-dake-hana-mazansu-kara-aure-aa-ayagi/
Aisha Ahmad Ismail ta kara da cewa, kungiyar ta yan Jarida ta KCJF a bude take ga hadin gwiwa da hukumomin gwamnati, kungiyoyi masu zaman kansu, kamfanoni, da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasara da dorewar gangamin.
“Manufarmu ita ce gina al’umma mai fahimta, inda lafiyar haila ba ta zama shinge ga karatu, walwala, ko cigaban ‘ya’ya mata,” ta jaddada.
Kungiyar ta yi kira ga jama’a da su tallafa wa #FlowPioneersKano ta hanyar bayar da pad na haila, shiga aikin sa kai, ko yada sakon gangamin domin fadada tasirin shirin.
Don Karin Bayani,kuma a iya Tuntubar wadannan mutanan:
Aminu Abdullahi Ibrahim – 07036968481
Dr. Abdulkadeer Ali Kurawa – 08035838452
Aisha Ahmed Ismail – 08065068974

