Ɗan Gwamnan Jihar Anambra, Chinua Soludo, ya ɗauki nauyin biyan kuɗin jinya na wasu marasa lafiya a asibitoci daban-daban da ke wasu ƙananan hukumomi uku na jihar, a wani mataki na taimakon jin-ƙai da ya yi a lokacin bikin Kirsimeti.
Chinua Soludo, wanda shi ne ɗan Gwamnan jihar, Farfesa Chukwuma Soludo, ya kai ziyarce-ziyarce ba tare da sanarwa ba zuwa wasu asibitoci a ranar Alhamis, inda ya tarar da marasa lafiya da ke fama da matsin rayuwa sakamakon rashin isassun kuɗaɗen jinya.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/kirsimatikudin-tikitin-jirgin-sama-ya-tasamma-naira-miliyan-1-a-najeriya/
A yayin ziyarar, ya biya dukkan kuɗaɗen jinyar wasu marasa lafiya, lamarin da ya kawo musu sauƙi da farin ciki, musamman a wannan lokaci na bukukuwan Kirsimeti.
Har ila yau, ya nuna tausayi da kulawa ga marasa lafiyar tare da ƙarfafa musu gwiwa su ci gaba da fatan samun lafiya.
Wasu daga cikin marasa lafiyar da ‘yan uwansu sun bayyana godiya da jin daɗinsu kan wannan mataki, suna cewa taimakon ya zo musu a daidai lokacin da suke cikin mawuyacin hali.

