Gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf ta tabbatar wa jama’a cewa jihar tana cikin cikakken tsaro, kuma babu wata barazana ga zaman lafinta.
A cikin sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar bayan taron Majalisar Tsaro ta Jihar da aka gudanar ranar Lahadi 30 ga Nuwamba tare da shugabannin hukumomin tsaro, ya jaddada cewa babu wani sahihin bayani da ke nuna barazanar kai hari ko tada hankali a Kano.
Gwamnati ta ce yaɗa jita-jita da labaran bogi da wasu ke yi domin tayar da hankalin jama’a babban laifi ne da zai jawo hukunci.
KARINLABARAI:https://tsthausa.com/gwamnatin-kano-ta-magantu-kan-zargin-dawowar-sanaar-achaba-a-birnin-kano-da-kewaye/
Gwamna Yusuf ya bayyana cewa dukkan hukumomin tsaro da na leken asiri suna aiki tare cikin tsauraran matakan sa ido da sintiri domin kare zaman lafiyar jihar.
A cewar sanarwar, an tura jami’an tsaro a sassa daban-daban na jihar tare da inganta tsarin sa ido domin dakile duk wani yunkurin tada hankali.
Gwamnatin ta kuma bukaci jama’a da su kasance masu hankali da biyayya a amfani da kafafen sada zumunta.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/kalaman-ganduje-na-kafa-hisba-da-na-barau-akan-cigaban-kano-su-ne-suka-janyo-rashin-tsaro-a-jihar-gwamnatin-kano/
Gwamna Yusuf ya tabbatar da cewa gwamnatin sa na ƙoƙarin kara karfafa tsaro ta hanyar inganta leken asiri, haɗin kan hukumomi, da amfani da sabbin dabarun zamani wajen kare jihar.
Gwamnati ta sake nanata cewa Kano na da tsaro, kuma a shirye take ta kare kanta daga duk wata barazana.
An bukaci jama’a da su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin kwanciyar hankali.

