Close Menu
  • Shafin Farko
  • Labarai
  • Ketare
  • Siyasa
  • Noma da Kiwo
  • Yanayi
  • Tsaro
  • Karin Wasu
    • Kasuwanci
    • Ilimi
    • Nishadi
    • Muhalli
    • Lafiya
    • Ra’ayi
    • Wasanni
Facebook X (Twitter) Instagram WhatsApp Telegram
TST HAUSATST HAUSA
  • Shafin Farko
  • Labarai

    RAMADAN: Gwamnan Sokoto Aliyu ya bada umarnin Fara Biyan Ma’aikatan Jihar Albashin Fabareru nan Take

    February 12, 2026

    An Gudanar da Sallar Rokon Ruwa a Saudiyya

    February 12, 2026

    HAJJ 2026: Hukumar Alhazan Kano ta Sanar da Ranar Fara Allurar Rigakafi da Binciken Lafiyar Maniyyata

    February 7, 2026

    Najeriya ta Kashe Sama da Naira Tiriliyan 7 a Bangaren Wutar Lantarki, Amma har Yanzu Ana Fama da Duhu — Rahoto

    February 7, 2026

    HUDUBA:Matasan Yanzu Idon su ya Rufe da Neman Kudi, Shiyasa Suke Saka Kansu a Caca da Crypto – Dr. Abdullah Gadon Kaya

    February 6, 2026
  • Ketare

    Yau Ake Toshe Shafukan Sada Zumunta na Yara yan Kasa da Shekara 16 a Australia

    December 4, 2025

    Rikicin Gaza:Sarkin Saudiyya ya amincewa Falasdinawa 1000 su shiga kasar su sauke farali kyauta

    May 19, 2025

    Duk wanda ya yarda zai bar Amurika ya koma kasarsa zamu bashi kyautar Dala 1000 – Inji Trump

    May 6, 2025

    Ba a ga jinjirin watan Shawwal a Saudiyya ba

    March 29, 2025

    An ga watan Sallah karama a Saudiyya

    March 29, 2025
  • Siyasa

    Majalisar Dokokin Kano ta Magantu kan Bukatar Mataimakin Gwamnan Jiha Aminu Gwarzo Ya yi Murabus

    January 31, 2026

    Shafin Kwankwasiyya Reporters a Facebook Ya Sauya Suna Zuwa Gida Gida Reporters

    January 26, 2026

    Yanzu Yanzu :Yan Majalisar Dokokin Rivers sun fara shirin Sauke Gwamnan jihar Fubara da Mataimakiyarsa daga Mulkin Jihar

    January 8, 2026

    Gwamna Yusuf Na da ‘Yancin Barin NNPP Zuwa APC kamar yadda Kwankwaso ya Bar PDP Zuwa NNPP – Shekarau

    January 6, 2026

    Dole ka daina tsoma Baki a harkokin APC, Ba zamu Bari Yadda ka Rusa PDP ka yiwa APC haka ba – Sakon Hotoro ga Wike

    January 6, 2026
  • Noma da Kiwo

    Za’a samu ƙarancin shinkafar Basmati da Indiya ke nomawa a bana

    September 4, 2025

    Tsadar rayuwa: Komai matsayin mutum a Najeriya ya koma gona,saboda abinda na hango -Inji wani Lauya

    December 15, 2024
  • Yanayi
  • Tsaro

    Duk wanda ya Kashe Wani a nemi shawarar Malamai a aika shi Lahira Kawai – Sheikh Daurawa

    January 18, 2026

    An sako Yan Mauludi 28 da aka sace tun 2025 a Filato

    January 10, 2026

    An Sace Amarya da Kawayenta 14 a Sokoto ana Tsaka da Shagalin Biki Yau Lahadi

    November 30, 2025

    RASHIN TSARO: Gwamnonin Katsina da Plateau sun rufe makarantun jihar nan take

    November 21, 2025

    Yan Najeriya su koyi kokawa da Dambe domin kare kansu daga yan bindiga -Inji Christopher Musa

    August 23, 2025
  • Karin Wasu
    1. Kasuwanci
    2. Ilimi
    3. Nishadi
    4. Muhalli
    5. Lafiya
    6. Ra’ayi
    7. Wasanni
    8. View All

    Yan Najeriya basa shayin kashe Kudi, sunyi amfani da Fetur na Naira Tiriliyan 1.58 a Bikin Kirsimeti -In Ji Gwamnatin Tinubu

    January 22, 2026

    Dangote ne ya rage farashin fetur da kaso 5.6%, shi ya sa farashi ya sauka ba saboda janye harajin 15% ba.

    November 19, 2025

    Dangote ya buɗe sabon kamfanin siminti mai darajar CEFA biliyan 100 a Côte d’Ivoire

    October 13, 2025

    Dangote ya ƙaddamar da gina kamfanin takin zamani na dala biliyan 2.5 a Habasha

    October 4, 2025

    Marubuciyar Najeriya, Dr Asma’u Isah Maibasira, Ta Kaddamar da Littafin Jagoranci a Birtaniya

    February 7, 2026

    An yi taron Murnar cika shekaru 30 da samar da Cibiyar addini ta Usman bn Affan Gadon Kaya wacce Marigayi Sheikh Ja’afar ya Kafa

    February 1, 2026

    Wasika zuwa ga Gwamnan Kano kan bukatar Samar da Tsaro a makarantu ko Rufe su – Tsohon Kwamishinan Ilimi Sunusi Kiru

    November 24, 2025

    ASUU ga Gwamnati: Idan kuna da tsarin “ba aiki, ba albashi”, mu ma muna da “ba albashi, ba aiki

    November 17, 2025

    An Amince da Fara Shirya Fim ɗin Maitatsine – Darakta

    January 9, 2026

    Karamin Yaron da Kakarsa Ta yi Sanadiyar Daukakarsa a Duniya ya Cika Shekara 12

    December 14, 2025

    MUTU KA RABA — HISBA ta ce aure tsakanin Mai Wushirya da ‘Yar Guda ba ta dauke shi da wasa ba

    October 21, 2025

    Majalisar Yara: Gwamna Yusuf ya baiwa yara aron zaman majalisar zartaswarsa a Kano dan girmama Ilimi

    January 13, 2025

    Majalisar dokokin Kano ta amince da dokar cin tarar kuɗi ga duk wanda ya sake tofar da yawu ko majina akan hanya

    February 3, 2025

    Sauyin Yanayi: Gwamnatin Kano ta dauki sabbin matakan kare Muhalli

    January 31, 2025

    Daga yanzu an daina barin tilin shara akan titunan birnin Kano – Gwamnatin Kano

    January 13, 2025

    Da ’Yan Najeriya Sun San Haɗarin Abincin da Ake Shanyawa a Gefen Hanya, Ko Kyauta Aka Ba Su Ba Za Su Ci Ba — Masana

    January 30, 2026

    WHO Ta Yi Kira Da A Kara Haraji Kan Barasa Da Abubuwan Sha Masu Dauke Da Sikari

    January 14, 2026

    Tinubu Naira 10,400 kacal ya warewa kowane ɗan Najeriya a fannin lafiyarsa cikin kasafin kuɗin 2026 – NMA

    December 29, 2025

    Gwamna Yusuf ya amince da Kashe kuɗi naira miliyan 164 domin sake gyara Asibitin Asiya Bayero

    November 2, 2025

    Ya kamata Hisba da Malamai a Kano su bayyana matsayinsu kan yadda yan siyasa ke jifan juna da kalmar LUWADI – Anas Hassan

    February 24, 2025

    Labarin dan Jaridar da ya kafa tarihi a duniyar yada labarai a kafar sadarwa ta zamani

    February 3, 2025

    Burinmu a yanzu shine Barau FC ta samu gurbin shiga gasar zakarun Nahiyar Africa – DSP Barau

    February 25, 2025

    An karrama jagoran kwallon kafa na Barau Jibiril Academy da lambar gwarzon shekara a bangaren Shugabanci

    December 21, 2024

    RAMADAN: Gwamnan Sokoto Aliyu ya bada umarnin Fara Biyan Ma’aikatan Jihar Albashin Fabareru nan Take

    February 12, 2026

    An Gudanar da Sallar Rokon Ruwa a Saudiyya

    February 12, 2026

    Marubuciyar Najeriya, Dr Asma’u Isah Maibasira, Ta Kaddamar da Littafin Jagoranci a Birtaniya

    February 7, 2026

    HAJJ 2026: Hukumar Alhazan Kano ta Sanar da Ranar Fara Allurar Rigakafi da Binciken Lafiyar Maniyyata

    February 7, 2026
TST HAUSATST HAUSA
Home » Hukumar KSSSMB na yiwa sabon shugabanta Gwarzo maraba ,Amma ba za’a manta da gudun mowar Dr. Bello Shehu ba – Nababa
Ilimi

Hukumar KSSSMB na yiwa sabon shugabanta Gwarzo maraba ,Amma ba za’a manta da gudun mowar Dr. Bello Shehu ba – Nababa

By tstDecember 16, 20244 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
IMG 20241216 WA0033

Daga Adamu Muhammad Nababa.

GUGUWA A CIKIN KAFO SHAYI !!!

Lallai ranar Lahadi 15 /12/2024 rana ce mai tarihi da haske a bangaren Ilimi a Kano gata Kuma tazo ƙarshen mako wacce ta dace da ranar karshen ta hutun da su kansu dalibai keyi.

A bangarena nima na himmatu da hutun karshen mako Ina karanta jaridu kawai Sai idona ya tsinci kanun jaridar Daily Nigerian da Jaafar Jaafar ya wallafa na cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya sauyawa wasu shugabanni wuraren aikinsu hakan yasa na gyara zama sosai.

Ba a gama mantawa da abinda ya faru ba na ranar Alhamis wato sauye-sauyen da aka samu a Majalisar zartaswa ta gwamna inda Gwamna ya ba wa irin su Sagagi da Bichi takalma su saka su kara gaba.

Sai kwatsam Kuma wani abokin aikina ya kira ni ya ce an samu canji a wasu hukumomin jihar da Gwamna ya sakeyi.

Sai ya aiko min da Sanarwa na Jaridu suka wallafa cewa an dauke Kabiru Ado Zakirai, daga hukumar kula da makarantun sakandire ta kano wato KSSSMB zuwa dakin karatu na gwamnatin jiha.

Kafin na tambayeshi wa aka kawo kuma,sai ya turon sunan Hon Rabiu Sale Gwarzo da zai maye gurbinsa.

Samun labarin hakan sai naji kamar wani juyin mulki akayi a kasar da ake mulkin kama karya.

A zahirin gaskiya bamuyi mamaki ba Kuma dama mun dade Muna cewa kamar wanda ya tafi, bai shirya ba,ya karbi matsayin da aka bashi Wasu ma na zargin bai dace ba kuma bai cancanta ba.

Bugu da kari dan kadan ya sani game da Hukumar, haka abubuwa sukaita tafiya har saida shi kansa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fahimci matsalar da kansa.

Wannan hukuma ta KSSSMB ba hukuma bace da za’ayi wasa da ita ba .

JAGORANCIN JAGORA

Ina da sha’awa ta musamman kan wannan rubutu domin kuwa Zakirai ya kasa baiwa KSSSMB shugabancin da ake bukata domin hukumar ta cimma muradun ilimi da aka sa gaba.

Duk yadda ake bashi shawarwari yaki dauka saboda ma daukar kansa yake kamar Wanda ya kware a bangaren ilimi ,to Amma abinda muka sani shine komai nisan gona akwai kunyar karshe Kuma yau anga kunyar karshe

WACCE RAWA SHUGABANNNI HUKUMAR KSSSMB SUKA TAKA A BAYA?

Hukumar KSSSMB ta doru akan saiti bayan da ta hadu da mai jini a jika dan shekara 41 mai karatun digiri na uku (PhD) Wanda Kuma ba kowa bane illa Dr Bello Shehu wanda kuma yasan makamar aiki yayi duk mai yiyuwa wajen daga darajar hukumar ta KSSSMB.

Kafin zuwan Dr Bello Shehu, hukumar ta kuma samu Shugaba irinsa mai digirin digirgir Wato Dr Husaini Abdullahi Ganduje,Kuma Shima anga irin rawar da ya taka wajen daga darajar hukumar.

Hukumar ta KSSSMB ba kuma zata manta da gudun mowar da Hon Habib Hassan El-Yakub ya taka wajen ciyar da Hukumar gaba kasancewarsa Shima goga ne yasan hanya irinsu Dr Bello Shehu.

SAUYI BA TSAMMANI

A wannan lokaci bayan hukumar ta KSSSMB ta dauki tsawon shekara daya da watanni tana cikin wani hali,a gefe daya kuma ana ta yiwa gwamna rufa rufa a bangaren Ilimi,sai kwatsam ya gwamna ya gaggauta ceto bangaren Ilimi baki dayansa daga neman lalacewar da ya dauko aka sauya Shugaban hukumar ta KSSSMB bayan shi kansa kwamishinan ilimi na Kano da aka sauya .

To me ya ragewa hukumar a yanzu shine sai a sake zuba Ido dan ganin abinda Sabon shugabanta Hon Rabiu Sale Gwarzo yazo dashi .

Wasu na ganin da gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf bai gaggauta ceto ilimin kano daga neman durkushewa ba to fah da duk burin gwamnan na fifita ilimi zai kare ne wajen fifita kashin Kai daga wasu da ake ganin shafaffu da mai ne musamman yadda ya ware kaso 31 cikin dari a kasafin kudin shekarar 2025 da sai shekarar ta kare Babu abin Azo a gani.

Tunasarwa ga duk Wanda zai rike hukumar KSSSMB da sauran hukumomin ilimi su gane cewa ilimi rai ne dashi kana shakeshi sai jiki ya gane .

Na gode

Share. Facebook Twitter Email Telegram WhatsApp

Related Posts

Marubuciyar Najeriya, Dr Asma’u Isah Maibasira, Ta Kaddamar da Littafin Jagoranci a Birtaniya

February 7, 2026

An yi taron Murnar cika shekaru 30 da samar da Cibiyar addini ta Usman bn Affan Gadon Kaya wacce Marigayi Sheikh Ja’afar ya Kafa

February 1, 2026

Wasika zuwa ga Gwamnan Kano kan bukatar Samar da Tsaro a makarantu ko Rufe su – Tsohon Kwamishinan Ilimi Sunusi Kiru

November 24, 2025

ASUU ga Gwamnati: Idan kuna da tsarin “ba aiki, ba albashi”, mu ma muna da “ba albashi, ba aiki

November 17, 2025
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

SABBIN LABARAI

RAMADAN: Gwamnan Sokoto Aliyu ya bada umarnin Fara Biyan Ma’aikatan Jihar Albashin Fabareru nan Take

February 12, 2026

An Gudanar da Sallar Rokon Ruwa a Saudiyya

February 12, 2026

Marubuciyar Najeriya, Dr Asma’u Isah Maibasira, Ta Kaddamar da Littafin Jagoranci a Birtaniya

February 7, 2026

HAJJ 2026: Hukumar Alhazan Kano ta Sanar da Ranar Fara Allurar Rigakafi da Binciken Lafiyar Maniyyata

February 7, 2026

Najeriya ta Kashe Sama da Naira Tiriliyan 7 a Bangaren Wutar Lantarki, Amma har Yanzu Ana Fama da Duhu — Rahoto

February 7, 2026
Advertisement
© 2026 TST HAUSA Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.