Babban limamin masallacin Juma’a na Usman Bn Affan dake Unguwar Gadon Kaya cikin karamar hukumar Gwale a Kano ,Dr. Aliyu Muhammad Yunus, ya ce tsarin Muslim–Muslim da gwamnatin Shugaba Bola Ahmad Tinubu ta zo da shi bai kawo sauƙin rayuwa ga yawancin Musulmai ba, illa ma ya ƙara tsananta musu matsin tattalin arziki da zamantakewa da rikice rikice.
Dr. Aliyu Yunus ya bayyana hakan ne a yayin gabatar da hudubarsa ta ranar Juma’a inda ya ce an yi amfani da addini a matsayin hujjar siyasa, amma bayan kafa gwamnati, ayyuka da manufofi ba su dace da alkawurran da aka yi wa jama’a ba, musamman talakawa Musulmi.
Malamin na tsokaci ne kan harin Amurika a jihar Sokoto da sunan kashe yan Ta’adda amma Dr.Aliyu Yunus yace ankai harin ne da wata manufa ta kare kiristoci a jihar.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/huduba-masu-hassada-munafunci-gulma-da-girman-kai-zuciyarsu-ba-ta-zama-lafiya-sheikh-mahmoud/
Ya nuna takaicinsa, yana mai cewa idan Manufar Amurika shine tabbatar da tsaro da kashe yan Ta’adda, meyasa Amurika din bata kai irin wannan hari a Zamfara da Katsina da wasu jihohi da ake kashe sauran mutane ba.
Sannan ya nuna mamakinsa kan yadda aka rufe shafin dan majalisar Amurika da ya bayyana dalilan kawo harin na Amurika zuwa Najeriya, wanda shima duk kokarinsa na daukar bayanan dan majalisar yaci tura.
Ya ce duk da cewa ana kiran gwamnatin Tinubu da sunan na Musulmi, wadannan matsaloli sun fi shafar Musulmai a matakin ƙasa, lamarin da ke nuna cewa suna kaɗai ba ya zama kariya ga jama’a.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/huduba-masu-yada-jita-jita-na-daga-cikin-wadanda-suka-hana-najeriya-zama-lafiya-farfesa-rijiyar-lemo/
Malamin ya jaddada cewa Musulunci bai yarda da zalunci ko cutar da talakawa ba, yana mai cewa adalci, gaskiya da tsoron Allah su ne ginshiƙan shugabanci nagari.
A cewarsa, duk shugabancin da bai tsaya kan waɗannan ka’idoji ba, ko da sunan Musulunci aka ɗora masa, sakamakonsa wahala ne ga al’umma.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/hudubamasu-zuwa-sallar-jumaa-ba-tsafta-na-cutar-da-su-kansu-malaiku-dr-bashir-aliyu/
Dr. Aliyu Yunus ya kuma yi kira ga al’umma da kada su ruɗu da laƙabi ko tsarin tikitin zaɓe kawai, sai dai su riƙa auna shugabanni bisa aiki,da gaskiya da tasirin manufofinsu a rayuwar talaka.
Ya buƙaci shugabanni da su duba halin da jama’a ke ciki tare da ɗaukar matakan da za su rage wahalhalun rayuwa, yayin da ya bukaci al’umma su dage wajen neman shugabanci na adalci da riƙon amana.
Sannan ya nemi jama’a su koma ga Allah, sannan su dage da adu’a da rungumar addinin Musulunci yadda ya kamata.

