Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya karɓi daruruwan yan jam’iyyar APC daga mazabar tsohon gwamnan jihar Kano kuma tsohon Shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr Abdullahi Umar Ganduje wato garin Dawakin Tofa daga APC zuwa jam’iyyar NNPP mai alamar littafi.
A yayin taron da aka gudanar a fadar gwamnatin Kano gwamna Yusuf ya bayyana farin cikinsa tare da cewa wannan mataki na sauya sheka ya nuna irin nasarorin da gwamnatinsa ta cimma a cikin shekaru biyu da suka gabata.
Ya bayyana garin Dawakin Tofa a matsayin muhimmin gari a fafutukarsa ta siyasa tare da yabawa Jagoran NNPP na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, bisa goyon bayansa.
Gwamnan ya jero wasu muhimman ayyuka da aka kammala a Dawakin Tofa, ciki har da ginin hanyar kilomita biyar da gwamnatin baya ta bari , tare da alkawarin gina sabuwar makaranta a garin na Dawakin Tofa.
Ya tabbatar wa sabbin yan jam’iyyar NNPP din cewa za a tafi da su ba tare da nuna wariya ba.
Har ila yau, gwamna Yusuf ya sanar da shirin mayar da kasuwar Dawanau ta kasa da kasa zuwa wata hukuma da za’a nada mata shugabanci kamar Manajan Darakta da kwamitin gudanarwa domin inganta harkokin kasuwanci.
TST Hausa ta rawaito cewa gwamna Yusuf ya kuma yaba wa Shugaban Karamar Hukumar Dawakin Tofa bisa tara naira miliyan 500 daga cikin gida da aiwatar da muhimman ayyuka da kudaden.
Shugaban karamar hukumar, Hon. Anas Danmaliki, ya ce an kammala ayyuka a makarantu 15 na firamare tare da daukar nauyin dalibai sama da 1,000 a manyan makarantu.
Shugaban NNPP na jiha, Hon. Hashim Dungurawa, ya taya sabbin yan jam’iyyar NNPP din murna tare da hasashen cewa jam’iyyar za ta yi fice a Dawakin Tofa a zaben 2027.
Jagoran NNPP a Dawakin Tofa, Alhaji Ahmad Muhammad Speaker, ya bayyana cewa da yawa daga cikin masu sauya shekar sun shiga jam’iyyar da kansu, tare da kiran a kammala wasu ayyukan da aka bari a Dawanau da Tumfafi.

