Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya taya Kwamared Auwal Bello Isma’il Danhajiya murnar zama sabon shugaban kungiyar sufuri da daukar ma’aikata ta RTEAN mai lakabin EMPLOYER reshen Jihar Kano.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren kungiyar, Kwamared Tijjani Ahmad, ya fitar.
Sanarwar ta ce mataimakin gwamnan ya yi wannan yabo ne lokacin da sabon shugaban ya kai masa ziyarar ban-girma a ofishinsa da ke Gidan Gwamnati, inda ya gabatar da sabbin manufofin da shugabancinsa zai aiwatardom in inganta harkokin sufuri a jihar.
Kwamared Danhajiya ya yi alkawarin yin aiki tare da Gwamnatin Kano domin daukaka ayyukan sufuri, tare da neman gudummawar gwamnatin Abba Kabir Yusuf wajen tsaftace tashoshin mota, gyara su, da samar wa matasa ayyukan yi.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, mataimakin gwamnan ya tabbatar wa kungiyar cikakken goyon bayan gwamnatin Kano domin habaka harkokin sufuri da ci gaban kungiyar a fadin jihar.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da manema labarai, shugaban kungiyar sufuri da daukar ma’aikata ta RTEAN (EMPLOYER) na kasa, Alhaji Dr. Musa Muhammad Maitakobi, ya tabbatar da ingancin zaben Kwamared Auwal Bello Isma’il Danhajiya a matsayin shugaban kungiyar na Kano.
Ya ce zabukan da aka gudanar a Kano da wasu jihohin Kaduna, Adamawa, Yobe, Neja da sun gudana bisa tanadin kundin tsarin mulkin kungiyar tare da kulawar jami’an tsaro, kafofin yada labarai, da masu ruwa da tsaki, bayan karewar wa’adin tsohon shugabancin a watan Oktoba 2025.
Dr. Maitakobi ya zargi wani tsohon sakataren kungiyar ta kasa da hada baki da wasu domin shirya zaben bogi a Kano, duk da gargadin da shugaban DSS ya yi lokacin tattaunawar sulhu da bangarorin da ke rikici, inda ya ja hankalin kowa da ya kiyaye doka da zaman lafiya.
Ya ce babu wata matsala a sauran jihohin da aka zabi sabbin shugabanni, sai dai a Kano inda wasu ke kokarin haifar da sabani.
Shugaban na kasa ya ce yana shirin amsa kiran Gwamna Abba Kabir Yusuf domin tattaunawa kan sabanin da ya taso a Kano, yana mai cewa a matsayinsa na dan Kano, ba zai so a samu rikici ko rashin zaman lafiya ba.
Ya bayyana cewa ya samu nasara a manyan kotuna biyu kan korafe-korafen da wasu ke yi wa shugabancinsa, lamarin da ya tabbatar da cewa masu kalubalantar ba su da hujjoji.

