Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya ce yana girmama hukumomin gwamnati da ita kanta doka, amma ya jaddada cewa dole ne a tabbatar da yin abin da ya dace a kowane lokaci.
Wike ya bayyana haka ne yayin da yake mayar da martani ga masu sukarsa da yin cece-kuce kan abinda ya faru tsakaninsa jami’an tsaro na sojojibi a Abuja ranar Talata.
A cewarsa, yana da cikakken imani da tsarin doka da oda, amma bai kamata a bari wasu su take ƙa’idoji ko su yi abin da suka ga dama ba tare da hukunci ba.
“Ina girmama hukumomi, amma dole ne a tabbatar da yin abin da ya dace, Ba zan yi shiru idan aka yi abin da bai dace ba,” in ji Wike.
A wani taron manema labarai da Wike ya kira a ofisoshinsa ranar Alhamis,yace zaici gaba da aikinsa akan doka Kuma ba zaija da baya ba.
Wannan martanin na Wike ya zo ne bayan jama’a da dama sun rika sukar yadda ya yi mu’amala da sojan ruwa Yarima a wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta.
Gidan Talabijin na AIT ya ruwaito cewa Ministan ya yi kira da a ci gaba da mutunta dokoki da kuma kare martabar gwamnati, tare da tabbatar da gaskiya a dukkan lamura.

