Gwamnatin Jihar Kano ta haramta kafa kowace ƙungiya ta Hisba mai zaman kanta a Jiha r.
Kwamshinan Yada Labarai na jihar Kano Kwamared Ibrahim Abdullahi Wayya ne ya bayyana hakan a madadin gwaman Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf a wani taron manema labarai.
Ya ce kamar yadda dokar kafa hukumar ta Hisba da aka yiwa gyara a shekarar 2005 Haramun ne a sake kafa wata hukumar Hisba guda biyu a jihar.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/mun-samar-da-hisba-gandujiyya-ba-don-fito-na-fito-da-gwamnati-baza-mu-kaiwa-gwamna-ziyara-domin-neman-albarka-sheikh-ib
Kwamshinan ya ce kafa hukumar ta Hisba Fisabillalahi da tsohon gwaman Kano Dr. Abdullahi Ganduje zai kafa ya saba dokar kasa.
A cewar gwanantin Kano Hisba da ke ƙarƙashin Gwamnatin Kano ita ce kadai hukuma mai lasisi da hurumin gudanar da ayyukan tsaro da kula da ɗabi’a bisa tsarin da aka tanada.
Don haka, duk wani ƙoƙari na wasu kungiyoyi ko mutane na kirkirar sabuwar Hisba za a ɗauke shi a matsayin karya doka.
Gwamnatin ta kuma gargadi al’umma da su guji shiga kungiyoyin da ba su da sahalewar gwamnati, tare da tabbatar wa jama’a cewa za ta ci gaba da daukar matakan da suka dace domin tabbatar da zaman lafiya da bin doka a fadin jihar.
KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/kalaman-ganduje-na-kafa-hisba-da-na-barau-akan-cigaban-kano-su-ne-suka-janyo-rashin-tsaro-a-jihar-gwamnatin-kano/
Haka zalika, gwamna Yusuf ya bukaci malaman addini, da shugabannin al’umma da masu ruwa da tsaki da su taimaka wajen wayar da kan jama’a kan illolin kafuwar kungiyoyin da ba su bi ka’ida ba, domin kaucewa rikice-rikice da tashin hankali a cikin al’umma.
Daga nan ya nemi Masu Ikirarin kafa hukumar Hisba Fisabillalahi da su janye kudurin ba tare da bata lokaci ba.
Sannan Gwaman Kano ya ce ko kama sunan na Hisba Fisabillalahi Haramun ne inda ya ce Hisba Daya ce.

