Daga Malam Anas Idiris Hassan
Sannu a hankali bayan da duniyar yada labarai a sassa daban daban ke kara samun sauyi ciki harda Najeriya, kafafen sada zumunta na zamani na daga cikin wadanda suka fara sauya duniyar yada labarai a kowacce kasa.
Saidai a wasu lokata da dama masu amfani da kafar sada zumunta din sunfi maida hankali wajen yada labaran karya,da labaran da zasu haifar da rigima da sauransu wanda anfi zargin cewa yawanci wadanda basu da gogewa a aikin jarida sune sukafi maida hankali a irin wannan bangaren.
Kasashe irinsu Amurika da Indiya da Chaina da Rasha sune kan gaba wajen yada labaran karya a kafafen sadarwa na zamani musamman a lokutan zaben Kasashen,ta cikin wani rahoto da aka fitar a shekarar 2024.
Saidai akwai kasashen da suka tashi tsaye haikan wajen yaki da labaran karya,Kuma sukayi nasara kamar ,Kasar Barazil da Finland da Maxico da Norway da sauransu.
TST Hausa ta rawaito cewa duk da Najeriya bata cikin manyan kasashen duniya da suke fama da yada labaran karya a kafafen sadarwa na zamani amma kasar ta fuskanci kalubale mai yawa na yada labaran karya,musamman a duk lokutan zabe,Inda koda a zaben 2023 da ya wuce an yada labaran karya mai yawa da yake da alaka da zaben.
Misalin labaran karya da aka yada a game da zaben 2023 shine yadda wani dalibi mai shekara 23 dan asalin jihar Lagos ya yada labaran karya akan Peter Obi na jami’yar Labor party wanda yake neman takarar Shugabancin Najeriya,inda matashin ya wallafa cewa Peter Obi ya rabawa mabiya addinin kirista kudi a coci domin a zabeshi.
Sannan matashin ya yada cewa dan takarar Shugabancin Najeriya a jami’yar NNPP sanata Rabiu Musa kwankwaso bashi da digirin digir gir na karatu daga jami’a.
Daga baya duka yan siyasar suka karyata labarin.
Kafin nan a shekarar 2019 lokacin da Buhari yake neman wa’adi na biyu an yada cewa ya mutu a Asibtin da yake zuwa jiya a Burtaniya daga baya fadar Shugaban kasa ta musanta labarin.
A Najeriya din dai,anyi amfani da kafofin sadarwa na zamani wajen yada labaran karya game da cutar Coronavirus ,cutar da ta billa a China daga baya ta bazu sassan duniya.
Har yanzu Najeriya na fama da labaran karya a kafar sadarwa ta zamani musamman abinda ya shafi siyasa da tattalin arziki da koshin lafiya da zamantakewar jama’a.
Kuma duka wannan na fitowa ne daga kafar sadarwa ta zamani ga masu anfani da ita wadanda ake zargin basa samun horo na musamman.
Saidai da alama zuwan kungiyoyin masu yada labarai a kafar sadarwa ta zamani ya iya kawo sauyi a Najeriya.
Anan Arewancin Najeriya Kungiyar masu yada labarai a kafar sadarwa ta zamani wato Online Media ta zabi Kwamared Musa Muhammad daga jihar Kaduna a matsayin sabon shugabanta na kasa shiryar Arewa.
Muhammad ya samu kuri’u 287 inda ya kayar da abokin takararsa, kwamared Lynn Adda, tsohon shugaban Kungiyar yan jarida NUJ na jihar Taraba, wanda ya samu kuri’u 138.
Kwamared Femi Adi daga jihar Kogi shine ya zama babban sakataren Kungiyar da kuri’u 210 Inda ya kayar da kwamared Rayyan Al-Hassan, wanda ya samu kuri’u 207.
A jawabinsa na karabar ragamar Shugabancin Kungiyar na Arewa Kwamared Musa Mohammed ya bukaci ‘ya’yan kungiyar da ke jihohin Arewa 19 da su yi amfani da kafafen sada zumunta wajen yakar labaran karya da inganta shugabanci na gari.
A cewarsa, dandalin sada zumunta na yanar gizo na iya zama abin dogaro ne kawai don yada labarai lokacin da kwararrun ‘yan jarida suka karbe ragamar aiki tare da amfani dashi ta hanyar kwarewa.
Daga nan Kano kuma,babu hamayya ,saboda kwarewarsa da gogewarsa, Kungiyar ta zabi kwamared Abbas Yushe’u Yusuf a matsayin Ma’ajin kudi.
Abbas Yusuf ya kawo sauyi da dama bangaren yada Labarai a kafar sadarwa, Musamman kokarin fito da abu yadda yake da kuma sanar da gwamnati ko masu ruwa da tsaki abinda ke faruwa ba tare da jin tsoro ko shayi ba.
Babban cigaban da aka samu a kano shine zaburar da matasan yan jarida kan su kafa Jaridar yada labarai a kafar sadarwa, bayan kafuwar Jaridar Nigeria Tracker a ranar 30 ga watan Yuni na shekarar 2020 Kuma kusan itace kafar sadarwa ta biyu da tayi tashe wajen yada labarai mai inganci, Jaridar da Abbas Yusuf ya kafa bayan ya bar aiki da Freedom Radio a ranar 11 ga watan Maris na shekarar 2020.
An haifi Ma’ajin kuɗi na Kungiyar masu yada yada labarai a kafar sadarwa ta zamani Abbas Yusuf a watan Augusta a shekarar 1983 a garin Dan Madanho cikin karamar hukumar Gezawa.
Abbas,ya kammala karatunsa na nazarin aikin jarida (Digirin Farko)a jami’ar Bayaro dake Kano a shekarar 2008 sanan ya koma yayi digiri na biyu wato masters a bangaren na aikin jarida a shekarar 2017 a jami’ar ta Bayaro.
A halarci taron karawa juna sani akan aikin jarida a wurare daban daban a fadin Najeriya,sannan daga shekarar 2017 zuwa 2019 ya halarci taron karawa juna sani a jami’ar Northwest dake Kano kan fassara labarai.
Kafin nan Abbas Yusuf ya zamo daya daga cikin masu tace labarai a gidan Radio Freedom a shekarar 2017 zuwa 2020 bayan ya dawo daga gidan gwamnatin jihar Kano a matsayin wakilin gidan Freedom acan.
A watan Oktoban shekarar 2017 ne aka dawo da Abbas Yusuf daga gidan Freedom Radio bayan wani labari da ake zargin ya yada wanda baiyiwa gwamnatin Dr Abdullahi Umar Ganduje dadi ba ,wato kan harin da yace an kaiwa tawagarsa a hanyar Abuja, lokaci da takun saka ya fara zafi tsakanin bangaren Ganduje da Sanata Kwankwaso.
Sabon Ma’ajin kuɗi na Kungiyar masu yada labarai a kafar sadarwa ta zamani,ta Arewa Abbas Yusuf duka kafin nan shine dan jarida na farko da ya wakilci Rahma Radio farin cikin al’umma a gidan gwamnatin Kano a shakerar 2011 zuwa 2012 kafin ya koma Freedom Radio,kuma suka amince yaci gaba da zama a gidan gwamnatin daga shekarar 2012 zuwa 2017.
Bayan ya ajiye aikin yada labarai a Radio a shekarar 2020 ,Abbas Yusuf ya kafa gidan jarida na Nigeria Tracker Wanda shine Shugabanta.
A dalilin haka ne ya taba rike kujerar babban Sakataren Kungiyar masu yada labarai a kafar sadarwa ta zamani (Online Media) na kasa reshen Kano daga nan kuma a yanzu yake rike da Ma’ajin kuɗi na Kungiyar reshen Arewa mai jihohi 19 a sabon zaben da akayi a Kaduna.
Bayan kafa Jaridar Nigeria Tracker, Abbas Yusuf ya taimakawa marasa karfi da masu bukata ta musamman da gano wasu kura kurai da yan siyasa keyi a cikin gwamnati a Kano dama Najeriya da nufin gyara ko gano bakin zaren.
Har yanzu kuma ba’a sani ba ko Abbas Yusuf ya na da sha’awar shiga siyasa anan gaba.
Saidai a shekarar 2023 ya rike Daraktan yada labarai na kwamatin yakin neman zaben dan takarar gwamnan jihar Kano a jami’yar ADP Sha’aban Ibrahim Sharada.

