Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta sake baiwa gwamnatin tarayya wa’adin makonni hudu ta warware dukkannin jarjejeniyar da aka kulla da Kungiyar a shekarar 2009.
Kungiyar ta ASUU tace ba zata zura idanu gwannati da yan siyasa su lalala Ilimin jami’o’in Najeriya ba .
Shugaban Kungiyar Malaman jami’o’in Najeriya reshen Kano Farfesa Abdulkadir Muhammad ne ya bayyana hakan a taron manema labarai da Kungiyar ta kira a ofishinta dake jami’ar Bayero a Kano.
TST Hausa ta rawaito cewa, Kungiyar ta ASUU reshen Kano ta hada da jami’o’i guda 7.
Farfesa Muhammad yace a baya sun janye yajin aikin mako biyu da suka fara na gargaɗi ne bayan taron kwamatin zartaswa na Kungiyar da akayi a Abuja ranar 21 ga watan Oktoba.
Yace janye yajin aikin ya biyo bayan tuntuba da akayi daga kowanne bangare musamman ɗalibai da iyayensu da kungiyoyin kwadago da sauransu.
Farfesa Muhammad ya kuma yi martani kan yadda ake ci gaba da riƙe wa malaman jami’a albashi a duk lokacin da aka samu tsaiko ko yajin aiki, wanda ya ce hakan na jefa tsarin ilimi cikin babban haɗari.
ASUU ta ce wannan mataki na gwamnati na ci gaba da tauye haƙƙin malamai , tare da haifar da koma baya ga ci gaban jami’o’i da ingancin karatu.
Kungiyar ta jaddada cewa lokaci ya yi da gwamnati za ta cika alkawurran da ta dauka, na inganta yanayin aiki da walwalar malamai, tare da magance matsalolin da suka jawo rikice-rikicen da ya haifar da yajin aikin gargaɗi.
Kungiyar ta gargadi gwamnati cewa ba za ta ci gaba da gudanar da ayyuka ba tare da samun albashi ba, musamman idan bangaren gwamnati ya dage kan manufofin da ke cutar da ma’aikata da tsarin ilimi gaba ɗaya.
Daga nan ASUU tace rikewa ma’aikatan jami’o’i Albashi idan sun shiga yajin aiki ba zai razana su ba.
Haka Kuma Kungiyar ta gargaɗi gwamnatin tarayya kan yadda ake yawan kafa jami’o’i a Najeriya ba tare da an samar musu da tsari Mai kyau ba musamman kuɗaden gudanarwa.
A karshe Shugaban Kungiyar na ASUU reshen Kano Farfesa Abdulkadir Muhammad ya nemi masu ruwa da tsaki da suka hadar da Sarakunan gargajiya da Malaman Addini da kungiyoyin fararen hula da kungiyoyin kwadago da su ja hankalin gwamnati tayi abinda ya dace domin gudun kada Kungiyar ta sake rufe jami’o’in Najeriya,rufewar da babu ranar budewa sai anyi abinda ya dace.

