Daga Kola Oyelere, Kano
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya bukaci gwamnatin tarayya ta kirkiro manufofi da za su taimaka wajen tallafawa manoma,da karfafa bangaren masu zaman kansu tare da inganta masu noman shinkafa a fadin kasar.
Gwamnan wanda kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar, Alhaji Shehu Wada Sagagi, ya wakilta a yayin taron nuna kayan da masana’antu na cikin gida ke samarwa yace manoma na taka rawa wajen bunkasa tattalin arzikin kowacce kasa.
Taron Wanda na shekara-shekara ne kungiyar masana’antu ta Najeriya (MAN) reshen Kano da Jigawa ce ta shirya a birnin Kano.
Ya ce Jihar Kano na da gagarumin damarmaki wajen bunkasa tattalin arziki musamman a bangaren sarrafa kayan gona da cinikayya, inda ya jaddada cewa idan aka yi amfani da wannan damar yadda ya kamata, za ta zama ginshikin ci gaba ba ga jihar kadai ba, har ma da daukacin arewacin Najeriya.
Gwamna Yusuf ya yaba da baje kolin, yana mai cewa babbar dama ce ga masana’antun cikin gida kuma hanya ce ta kara bunkasa tattalin arzikin kasa baki daya.
Haka kuma ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da bai wa bangaren masu zaman kansu goyon baya a bangaren noma domin rage rashin aikin yi, tare da tabbatar da cewa Kano a bude take ga dukkan masu zuba jari na cikin gida da na waje.
Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika amfani da kayayyakin da aka kera a cikin gida, duba da irin rawar da suke takawa wajen bunkasa tattalin arziki da ci gaban kasa.
Gwamnan ya kuma bayyana cewa ana gudanar da tattaunawa tsakanin gwamnatin Kano da Jamhuriyar Chadi domin fadada harkokin zuba jari a kasuwar dabbobin jihar.
A nasa bangaren, shugaban kungiyar masana’antun Najeriya (MAN) reshen Kano da Jigawa, Alhaji Muhammad Bello Isyaku Umar, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta samar da yanayi mai inganci da zai karfafa wa masana’antu gwiwa.
Ya ce, “Tare da yawan jama’ar Najeriya da ya haura miliyan 200, gwamnati ba za ta iya samar da ayyukan yi ga matasa kadai ba.
Dole ne gwamnati ta gane irin rawar da bangaren masu zaman kansu ke takawa wajen samar da ayyukan yi da ci gaban tattalin arziki.
“Wannan kuma ba zai yiwu ba sai da manufofin da ke tallafawa masana’antu,da wutar lantarki mai araha, da kuma sauran abubuwan da za su karfafa ci gaban masana’antu domin su dauki karin matasa aiki “in ji Umar.

