Matatar Dangote ta fara sayar da hannun jarinta ga jama’a a yau Litinin, 14 ga Satumba, 2026, a wani mataki da zai bai wa miliyoyin ‘yan Najeriya damar mallakar wani kaso na matatar.
Kamfanin na neman sayar da hannun jari biliyan 4.1, a farashin Naira 525 kan kowane hannu, inda ake sa ran tara kusan Naira tiriliyan 2.15 idan an sayar da dukkan hannun jarin.
Masu shirya cinikin sun bayyana cewa ana sa ran jawo masu zuba jari kusan miliyan 10, abin da zai zama daya daga cikin manyan matakan faɗaɗa damar talakawan Najeriya shiga harkar kasuwar hannayen jari.
An kuma sauƙaƙa farawa, domin mutum zai iya sayen mafi ƙarancin hannun jari guda 10, wanda ke nufin zai iya fara zuba Naira 5,250.
Wannan ya bai wa ma’aikata, ’yan kasuwa da sauran masu ƙaramin jari damar shiga cikin mallakar kamfanin.
Kuɗin da za a tara daga hannun jarin za a yi amfani da wani ɓangare wajen faɗaɗa matatar, inda ake shirin ƙara ƙarfin sarrafa ɗanyen mai daga ganga 700,000 a rana zuwa ganga miliyan 1.4 a rana.
Ga masu zuba jari da mallakar hannun jarin na iya ba su damar cin gajiyar ribar kamfanin idan ya samu riba kuma ya raba wa masu hannun jari, ko kuma su samu ƙarin darajar hannun jarinsu idan farashinsa ya tashi a kasuwa.
Sai dai babu tabbacin riba ko cewa farashin hannun jarin zai tashi, don haka ana buƙatar masu zuba jari su fahimci haɗarin kasuwa kafin su saka kuɗinsu.
Aliko Dangote ya kuma ce ƙananan masu zuba jari za su samu fifiko wajen rabon hannun jarin, yayin da ya bayyana cewa farashin hannun jarin da aka fara bayarwa a Naira 525 na iya kaiwa Naira 10,000 nan gaba.
Wannan dai hasashe ne na Dangote, ba tabbacin farashin da hannun jarin zai kai ba.
