Gwamnatin jihar Kano ta bada umarnin kara lokacin rufe kasuwanni a Kano saboda azumin Ramadan na bana.

Shugaban hukumar kula da kasuwar sabon Gari a jihar Kano Alhaji Abdul-Bashir Husain shine ya bayyana hakan a ganawarsa da manema labarai a ofishinsa.

TST Hausa ta rawaito cewa kasuwannin da karin lokacin rufewar ya shafa sun hada da kasuwar Sabon Gari da Singa da kasuwar Galadima.

Alhaji Abdul-Bashir yace gwamnatin Kano ta kara lokacin rufe kasuwanni ne domin jama’a su samu damar yin hada hada yadda kamata.

“Mun kara mintuna 30 a kowacce rana na rufe kasuwannin guda uku saboda albarkacin watan azumin Ramadan”Inji Abdul-Bashir.

Yace a yanzu maimakon karfe 6 da ake rufe kasuwanni, za’a koma karfe 6:30 na yamma .

Shugaban hukumar kula da kasuwar ta Sabon Gari yace saboda sauyin yanayi,rana bata faduwa da wuri , shiyasa aka kara lokacin rufe kasuwanni,Amma za’a koma tsarin baya idan azumi ya wuce.

Abdul-Bashir B Husain ya kuma shida cewa bude kasuwanni guda uku wato karfe 8 na safe na nan daram.

Ya roki yan kasuwar da su baiwa gwamnati hadin kai wajen tabbatar da ana bude kasuwannin da rufe su a lokacin da aka tsara

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version