Dan Majalisar Wakilai mai wakiltar Rano, Kibiya da Bunkure, Rt. Hon. Kabiru Alhassan Rurum, ya nuna matuƙar alhini kan rasuwar fitaccen ɗan kasuwa Alhaji Bature Abdulaziz, wanda ya rasu a Kano.

Rt. Hon. Rurum ya bayyana marigayin a matsayin ginshiƙi a harkokin kasuwanci da bunƙasar tattalin arziki, inda ya ce gudunmawar da ya bayar za ta ci gaba da kasancewa abin tunawa a Kano da Najeriya baki ɗaya.

Haka kuma, Rt. Hon. Rurum ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano da kuma iyalan Fatima Abubakar, wadda aka kashe tare da ’ya’yanta guda shida a Dorayi Chiranchi, Karamar Hukumar Kumbotso.

KARIN LABARAI:https://tsthausa.com/matashin-da-ya-jagoranci-taaddancin-dorayi-shine-ake-zargi-da-kone-mata-biyu-a-tudun-yola-in-ji-yan-sanda/

Dan majalisar ya yi Allah-wadai da wannan mummunan aiki, yana mai kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta bincike tare da tabbatar da cewa duk masu hannu a laifin sun fuskanci hukunci bisa doka.

Ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da Ya jiƙan mamatan da rahama, Ya kuma ba iyalan da suka rasa nasu ƙarfin jure wannan babban rashi.

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version