Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya raba babura ga wasu ’yan jarida da ke aiki a fadar gwamnatin Kano a wani mataki na tallafa musu da kuma nuna godiya ga rawar da suke takawa wajen yada labaran gwamnati.

Mai taimaka wa gwamnan na musamman kan kafafen sada zumunta, Salisu Muhammad Kosawa, ya bayyana hakan a shafinsa na Facebook inda ya ce tallafin zai taimaka wajen saukaka musu zirga-zirga.

Wadanda suka ci gajiyar wannan tallafi sun hada da wakilan kafafen Rahma Radio, da Radio Kano da Radio Nigeria Pyramid da Nasara Radio da ARTV da kuma ma’aikata daga ma’aikatar yada labarai ta Kano .

Babban daraktan yada labarai na gwamnatin jihar, Kano Hon. Sanusi Bature Dawakin Tofa ne zai mika baburan a madadin gwamnan.

Daga cikin wadanda za su karbi baburan akwai:

Usman Gwadabe

Sani Surajo

Adamu Dabo

Tukur S. Tukur

Tijjani Sorondinki

Ibrahim Muazzam

Mubarak Ismail

Jabir Ali Dan Abba

Rabiu Sanusi

Muzammil Sanda

Khalid Yusuf

Jama’a a Kano sun yi maraba da wannan mataki tare da addu’ar cewa Allah ya saka wa gwamna da alheri, ya kuma dawo da shi akan mulki karo na gaba.

Ana sa ran na gaba za’a bada kashi na biyu har zuwa na uku ,domin kowa ya amfana.

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version