Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗin wasu mutane a hukumomin gwamnatin Kano.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Kano Alhaji Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Juma’a yace dadin mutanan ya fara aiki nan take.

Daga cikin wadanda aka naɗa sun hada da:

1.Dr.Bashir A Muzakkar a matsayin babban daraktan hukumar kula da bunkasa harkokin sadarwa (KASITDA) kafin nadinsa shine mai baiwa gwamna Yusuf shawara kan fasahar tattalin arzikin na zamani.

2.Kabiru Sa’idu Dakata a matsayin shugaban hukumar tallace tallace ta Kano.

3.Dr Fatima Abdul Abubakar wacce gwamnan jihar Kano ya amince a matsayin shugabar hukumar kare hakkokin jama’a da zamantakewarsu.

4.Eng Isyaku Umar Kwa a matsayin mataimakin daraktan hukumar kula da gidaje ta jihar Kano.

5.Hamisu Musa Gambo Dan Zaki a matsayin shugaban hukumar bada tallafin Karatu ta jihar Kano.

6.Barista Isma’ila Nasarawa , Shugaban cibiyar koyar da yaki da cin hanci da rashawa.

7.Kaftain Muhammad Bello Maigaskiya Gabasawa mai ritaya,a matsayin kwamandan kwalejin horas da harkokin tsaro .

Sanarwar tace , gwamna Yusuf ya taya mutanan murna tare da nuna ganawarsa akan su.

Ya bukace su da suyi aiki tukuru domin sauke nauyin dake kansu.

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version