Allah yayiwa fitaccen dan kasuwar Najeriya dake birnin Kano Alhaji Aminu Dantata rasuwa a daren ranar Juma’a.

Ya rasu ya na da shekaru 94 da haihuwa a duniya.

An haifi Marigayi Alhaji Aminu Dantata a ranar 19 Mayu na shekarar 1931 ya kuma koma ga Allah a ranar 28 ga watan Yuni na shekarar 2025.

Har zuwa yanzu ba’a sanar da lokacin jana’izarsa ba a hukumance .

Wata makusanciyarsa ta shaidawa TST Hausa cewa ,marigayin ya rasu ne a kasar Dubai.

Ya koma ga Allah yana da yaya 7 da jikoki da dama ,daga cikin yayansa akwai Alhaji Tajuddeen Aminu Dantata sai kuma dan Yar uwarsa fitaccen attijirin Afurika Alhaji Aliko Dangote.

Akwai karin bayani na tare

Share.
Leave A Reply Cancel Reply

Exit mobile version